Posts

Showing posts from June 3, 2021

MATSALAR AQEEDAH

 GASKIYA AKWAI MATTSALA!!!! Sau nawa kake zama domin Bincike ko sauraron Yadda zaka gyara Ibadarka?????          Sau dadama idan na kadaita sai nayita tunani dan ganeda lammarin gudanar addini agun wasun mu. Zakaji mutum nakiran kansa musulmi amma farillan alwala ma bai sani balle in ta 'baci ya gyara farillan sallah ma bai saniba balle inyayi Rafkanuwa yagyara. Ko na wanka ballema ilimin gyaransu.     Wayyoooni duniya ina zaki damune kowa kagani abinci kawai yake nema kokuma yadda zai huta ko yadda zaiji dadin duniya gaba. Saidai kash itakuma tafiyarnan da take gaban mu batta da rana. Kawai zuwa take kwatsam kara zube ba zato ba tsammani.     To taya zamu tara guzirin komawa ga mahaliccin mu domin samun hujja garemu aranar sakamako?     Ansa     Mukoma munemi ilimin addini mugyara ibadu da mu'amalarmu kafinnan musami hanyar tsira. Wani abin ban takaici shine yawanci mukan jahilci lammarin addini bawai don rashinsaba ...

MUSULMI GA SAKO

 MUSULMI ATASHI AKAFA DAULA DAN SAMUN INGANTACCEN RAYUWA inji Shahararren malamin salafiyyannan Sheikh Muhammad Adam Albany Zaria.    Hakika shugaba yayi wadannan maganganu da shawarwarin agurare Ma bambanta da majalisai dadama. Domin nuni garemu ga hanyar tsira. Dakuma koyi da magabata. Don samun rayuwa Mai inganci, da zamantakewar rayuwa Mai tsafta. Ba kamar yadda wasu ke daukar zancen awata mahanga. Da tunani irinta miyagun mutani ba.  Ga zancen malam;  Tsokaci kan batun malam:     Saidai haryanzu banji wani shahararren mutum daga cikin malamai ko shugabanni daga cikin musulmiba wanda ke karfafa Zancen. Duk da cewar maganan maganice na ciwon dayake damun musulmin duniya baki daya. Saidaima wasu daga cikin miyagun mutane dasuke fassara zancen da wani salo nadaban, tayadda suke kokarin cire ma'anar maganan na hakika su shigoda wani al'amari nadabam.      Gadai Maganan da malam yayi; Mal. Yace ''Yakamata musulmi su kafa daula Dan gujewa ...

QALUBALE GA RAYUWAR 'YAN MATA

 📝  ✍️ ISMAIL HUSSAINI ADAM SMART DAN AREWA    ******* GABATARWA ******* Assalamu alaikum warahmatullahi wabarkatuhu mai karatu.        Zanyi wannan rubutunne don nuni zuwaga yan uwana maza, domin kusan wa zaku auro ku kawo cikin gidanku, amatsayin abokiyar zama. Mata kuma su san dawa zasuyi qawance don gudun faďawa akomar halaka. Inda hali kutsaya kukaranta gabaki ďaya, domin zaka/zaki k'aru kuma inshaa Allahu zaku rabauta da waďannan zantuka nawa.       Ina bukatan addu'arku Allah ya haskaka qabarin mahaifina, dana mai karatu idan kuma suna raye, Allah yasa mugama dasu lafiya yakuma basu rabon cikawa da imani. Allah ka albarkaci rayuwar lahaifiyata da ayyukan alkhairi daku mumaďin gabaki ďaya. ******** 'YAN MATAN JAMI'A ********    Allah sarki rayuwarsu gwanin birgewane, saidai kuma abin tausayine awani bangaren, tayadda zaka samesu mafi yawancinsu akwai tsaftar jiki dana tufi. sannan sun san yakamata matuka, Saidai was...

NASIHOHINMU AYAU

 MU LE'KA MAKABARTA )> . AWANNAN GURIN- Wasu Rahama Suke Sha,  Wasu Kuma Dũkan Tsiya Suke Ci. . AWANNAN GURIN- Wasu Sun 'Kosa A Tashi Alqiyamah, Sabo da Ni'mar da Suka hango A Gidansu Na Aljannah. Wasu Kuma Roko Sukeyi Kada A Tashi Qiyamar Sabo da Azabar da Suka Hango Tafi Wacce Suke Ciki Bala'i, . AWANNAN GURIN- Mutanan Kirkin da Ke Cikinsa dana Banzan dake Cikinsa, Suna yin Nadamar Lokacin da Sukayi Hasarar Sa, . NA KIRKIN CUKINSU: Suna Yin Nadamar Ina ma Ace Gaba daya Lokutansu Sun Qarar dashi Akan Bautar Allah, Sabo da Sakamakon Alkairin Aikinsu da Suka fara Gani. . NA BANZANSU KUMA: Suna Yin iihu, da Kururuwa, da Cizon Yatsa, da Takaicin Qarar da Rayuwarsu da Sukayi Akan Aikin Banza. . NI, DA KAI AYANZU- Zãbi ya Rage Agremu, ga Irin Rayuwar da Muke Son yi Bayan Mutuwar Mu, . Ko dai Mu Zabi Rayuwar da Mala'iku Zasu yi ta Jibgan Mu, Kunamu da Macizai Suyi ta Saran Jikin Mu. Ko Kuma Mu Zabi Rayuwar da Zamu Samu Nishadi da Natsuwa Acikin Qabarin Mu. . Kada Dai M...