Posts

Showing posts from May 21, 2021

RAYUWA ABAR TSORO CE

  *BABU UZRI BAYAN MUTUWA* -  "Duk wani uzrin da bawa yake ƙunshe dashi a lokacin rayuwarsa ne kaɗai yake da ikon aiwatar dashi, yana mutuwa shikenan uzri ya ƙare, abinda mutum ya shuka shi zai girba" - "Bayan mutuwarka a lokacin da aka ɗauke ka izuwa makwancin ka, komai yana jin abinda kake faɗa ga masu ɗaukar ka, amma saidai su mutanen da suka ɗauke ka ɗin basa taɓa jin abinda kake faɗa" - "Ya kai miskĩni! Lallai ka sani cewa fa, a lokacin da ka mutu shikenan taka ta ƙare, bayan an ɗauke ka acikin makara babu wanda yake fuskantar halin da kake ciki balle ya karɓi ƙorafinka, face dabbobi ko bishiyoyi, sai kuma ubangijin taliƙai, to ka gabatarwa da kanka wani alkhairi wanda ba za kayi nadama ba bayan mutuwarka"

TARBIYYA A SHARI'ANCE

 Gabatar da Tarbiyyar Musulunci Da sunan. Allah mai yawan Rahama mai yawan jinkai, bayan haka:Saninku ne iyaye, malaman makaranta, da masu damuwa da gyara da kuma ci gaban al’umma cewa Tarbiyya ita ce tubalin ginin dan adam, ko dai tubalin gini, ko kuma tubalin toka. Duk wata tarbiyya da ba ta musulunci ba, ko wadda ta ci karo da ita, to tubalin gininta na toka ne, ko ba jima, ko ba dade sunanta rushashshiya, tarbiyyar musulunci ita ce daki-bari, kadaura babbar inuwa, kowa ya rabe ta sai ya huta, ballantana wanda ya tashi a cikinta. TO (1)Me ake nufi da Tarbiyya a Musulunci? Tarbiyya a Musulunci tana nufin “Gina cikakken Mutum Sannu a hankali; don bin umarnin Allah da na manzonsa, da neman yardar Allah, da samar masa da nagarciyar rayuwa duniya da lahira, bisa tsari irin na musulunci” (2)Menene hukuncin gina yaro Akan tarbiyyar Musulunci? Gina yaro akan tarbiyyar musulunci wajibi ne, kuma hakki ne daga daga cikin hakkokin yaro akan maifansa (ko walliyansa)Dalilai akan Haka: 1. Daga...

GUZIRINMU AYAU

  MU LE'KA MAKABARTA )> . AWANNAN GURIN- Wasu Rahama Suke Sha, Wasu Kuma Dũkan Tsiya Suke Ci. . AWANNAN GURIN- Wasu Sun 'Kosa A Tashi Alqiyamah, Sabo da Ni'mar da Suka hango A Gidansu Na Aljannah. Wasu Kuma Roko Sukeyi Kada A Tashi Qiyamar Sabo da Azabar da Suka Hango Tafi Wacce Suke Ciki Bala'i, . AWANNAN GURIN- Mutanan Kirkin da Ke Cikinsa dana Banzan dake Cikinsa, Suna yin Nadamar Lokacin da Sukayi Hasarar Sa, . NA KIRKIN CUKINSU: Suna Yin Nadamar Ina ma Ace Gaba daya Lokutansu Sun Qarar dashi Akan Bautar Allah, Sabo da Sakamakon Alkairin Aikinsu da Suka fara Gani. . NA BANZANSU KUMA: Suna Yin iihu, da Kururuwa, da Cizon Yatsa, da Takaicin Qarar da Rayuwarsu da Sukayi Akan Aikin Banza. . NI, DA KAI AYANZU- Zãbi ya Rage Agremu, ga Irin Rayuwar da Muke Son yi Bayan Mutuwar Mu, . Ko dai Mu Zabi Rayuwar da Mala'iku Zasu yi ta Jibgan Mu, Kunamu da Macizai Suyi ta Saran Jikin Mu. Ko Kuma Mu Zabi Rayuwar da Zamu Samu Nishadi da Natsuwa Acikin Qabarin Mu. . Kada Dai...

NASIHOHINMU AYAU

 YADDA IYAYE ZASU MAGANCE MATSALAR DAUKE DAUKE DA YARA KEYI TIN SUNA QANANA NASIHA (2022) A Babi na Tarbiyya Duk Abin Da Yaronki Ya Dauka Idan Bai Tambayeki Ba Sannan Bake Kika Bashi Ba To Ya Ajiye Abin Kuma Idan Da Wani Yaro a Kusa Ki Dauka Ki Bashi Shi Yaronnaki Ya Haqura Sai Wani Lokacin Kuma Sannan Ki Tuhumeshi Dan Meyasa Na Aje Abuna Ka Dauka Baka Tambayeni Ba ? Ki Nuna Rashin Jin Dadinki Akan Hakan Sannan Ki Ladabtar Dashi . Hikimar Hakan Malaman Tarbiyya Sukace Don Kada Ya Tashi Da Wannan Dabi'ar Ta Dauke Dauken Kayan Mutane Basu Bashi Ba Wadda Idan Ya Ginu Akan Wannan Dabi'ar Idan Ba Kuyi Wasa Ba Sai Iyayensa Sun Zubar Da Hawaye Saboda Munin Dabi'ar Da Suka Gagara Datse Masa Ita Tin Yana Qarami  Jama'a Kun Fahimta............?RAYUWAR AURE BA HUTU DA JINDADI BANE KAWAI HAQURI YAFI YAWA NASIHA (2020) Karku Dauka Rayuwar Aure Hutune Zalla Da Jindadi a'a Duk Wadda Ya Fahimci Haka Toya Fahimci Lamarin a Baude Aure Ibadah Ne Da Kuma Haqurin Da Yakai Qololuwa Don A...

NASIHOHI DAGA NA 2024 ZUWA NA 2026

MU DINGA NAZARI AKAN TAIMAKAWA ADDININ ALLAH NASIHA MUHIMMIYA (2026)   Kayi Nazari Dakyau Tinda Kake a Rayuwa Wanne Taimako Ka Taba Yima Addinin Allah Wadda Ko Bayan Ranka Zai Iya Zama Sadaqatuj Jariya Gareka Kuma Kaci Gaba Da Taimakawa Gwar Gwadon Iko Idan Kuwa Ka Bin Cika Kaga Babu Tofa Har Yanzu Kana Da Sauran Dama Wadda Baza Kayi Nadama Ba Sai Kayi Qoqari Ka Ginawa Kanka Alherin Dazai Bika a Qabari Wadda Zai Yalwata Makwancinka Saboda Haka Muyi Qoqari Mu Ginawa Kan Mu Alherin Dazai Bimu Qabari Ta Fuskar Yawan Taimako Zuwa Ga Addinin Allah Da Kuma Mabuqata Da Sannu Allah Zai Isar Zuwa Ga Mizanin Mu Amma Sai Munyi Haquri Mun Kuma Kawar Da Kayi Da Hudubar Shaidan Ta Fuskar Talauci Da Yake Bijiro Mana a Yayin Taimako Kafin Mu Iya Taimakawa Addini Har Mu Sami Ingantaccen Masauki a Qabari Jama'a Mun Fahimta..........? GATAN DA ADAN ADAM YA SAMU SHINE KASANTUWARSA DA YAYI A RAYE NASIHA [2025] Babu Shakka Duk Wadda Allah s.w.t Ya Barshi Yini Daya To Ba Qaramin Gata Yayi Ma...

SUNNAH TAFARKIN TSIRA

MAFAKAR SUNNAH AYAU!!! Daga 🖊📝Ismail Hussaini Adam +2349047958802 Haqiqah Babu batun Sonkai, Salafawa da 'yan izala sune ke da'awar sunnah Haqiqanin ta zallar madarar sunnah babu gauraye. Dalilin wannan rubutu nawa: Shine nuna mecece koyarwar aqeedar sunnah. Da manufar Izala da Salafawa akan sunna dakuma mecece asalin haqiqanin aqidar sunnah ********MECECE AQIDAH******** Aqidah: amahangar Arufai (Malamai)_ wata hanyace wacce mutane suka kebance yadda zasu yi addini karkashin wata mazhaba bisa fahimtar magabata na farko, Bugu da kariaqidah takasance abace wacce take a aikace da furincin baka banda qudirin zuci. Ma'ana Azuci ni musulmine kuma nayarda da dukkan shika_shikan musulunci ina aikatasu amma bisa mazhabar malikiyya. To idan hakane madogarata bani da Ikon tilasta maibin mazhabar shafi'iyyah ko ko hanafiyya. Bani damar cewa sai sunbi Hambaliyya Idan mukayi duba danganeda yanayi nayanzu yadda rayuwa tashige rudani yadda Ake kawo abubuwa daban ...

MATAKAN TARBIYYA AKASAR HAUSA

MATAKAN TARBIYYA Daga. Alqalamin Ismail Smart Dasunan ALLAH Mai RAHAMA Mai JINKAI. Haqiqa tarbiyya dolece a addinin mu na musulunci musan man ma na iyalanka/ki Domin ALLAH MADAUKAKI yana cewa: ﷽ یا أیهاالذین آمنو قو أنفسکم وأهلیکم نارا وقودها الناس والحجارة Awannan aya ALLAH yayi umarni ga Muminai dasu Kare kansu da iyalansu daga wata wutta Wanda yakasance makamashinta mutane ne dakuma duwatsu. ALLAH UBANGIJI katsaremu amin ya RABBI. Awannan 'Bangaren Nakeson nayi rubutu domin yan uwa musulmai su anfana. ALLAH MADAUKAKIN SARKI ya dafamin MATAKIN FARKO (Neman Aure zuwa da yakai 5yrs) Dole Akan kowa Idan yazo neman aure Yanemi Mai addini Da hali nagari Da kakkyawar zuciya. Ba kawai kyawun fuskaba ko wani martaba ko nasabar Abokin zama ba. Kuma yazamto anyi auren tanasonsa yana sonta. Domin hakanne Zaisa suji dadin zamantakewarsu ta Aure Kuma hakan Zaisa yayansu sutaso dason junansu Da Bin doka ko umarnin Da akayi masu. Domin kada yazamto uwa tace fari uba yace Bahakaneba Baki yake. ...

Musulmin Nigeria Ga Shawara

MUSULMI ATASHI AKAFA DAULA DAN SAMUN INGANTACCEN RAYUWA inji Shahararren malamin salafiyyannan Sheikh Muhammad Adam Albany Zaria. Hakika shugaba yayi wadannan maganganu da shawarwarin agurare Ma bambanta da majalisai dadama. Domin nuni garemu ga hanyar tsira. Dakuma koyi da magabata. Don samun rayuwa Mai inganci, da zamantakewar rayuwa Mai tsafta. Ba kamar yadda wasu ke daukar zancen awata mahanga. Da tunani irinta miyagun mutani ba. Ga zancen malam; Tsokaci kan batun malam: Saidai haryanzu banji wani shahararren mutum daga cikin malamai ko shugabanni daga cikin musulmiba wanda ke karfafa Zancen. Duk da cewar maganan maganice na ciwon dayake damun musulmin duniya baki daya. Saidaima wasu daga cikin miyagun mutane dasuke fassara zancen da wani salo nadaban, tayadda suke kokarin cire ma'anar maganan na hakika su shigoda wani al'amari nadabam. Gadai Maganan da malam yayi; Mal. Yace ''Yakamata musulmi su kafa daula Dan gujewa hadarin dake gabansu, na miyagun ...